LabaraiUncategorized

Fadar Sarkin Musulmin Najeriya ta ce Talata za a fara duba watan Shawwal

Fadar Sarkin Musulmin Najeriya ta ce Talata za a fara duba watan Shawwal

Kwamitin ganin wata na Fadar Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III ya buƙaci al’ummar musulmin ƙasar su fara dibon watan Shawwal a ranar Talata

Kamar yadda bbchausa na ruwaito.Sanarwar da kwamitin ya wallafa a shafinsa na Twitter ya ce Talata ta kama 29 ga watan Ramadan daidai da 11 ga watan Mayu.

Majalisar Ƙoli ta Musulmi a Najeriya, NSCIA ta ce idan har Allah ya sa an ga watan, Sarkin Musulmi zai bayar da sanarwar ayyana Laraba a matsayin 1 ga watan Shawwal.

“Amma idan ba a ga wata ba ranar Talata, to kai tsaye Alhamis za ta kasance ranar Sallah a matsayin 1 ga Shawwal,” in ji sanarwar da NSCIA ta fitar a Twitter.

 

Bisa al’ada idan an ga watan ana sanar da Mai Gari ko Hakimi mafi kusa wanda kuma zai sanar har zuwa fadar Sarkin Musulmi.

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button