Labarai

Yanzu-Yanzu: Mutunen da ke kula da ƙabarin Manzon Allah ya rasu

Allah Ya yiwa mutumin da ke kula da ɗakin da kabarin Manzon Allah (SAW) yake a Masallacin Madina, Sheikh Abdou Ali Idris rasuwa kamar yadda aminiya ta ruwaito.

Agha Abdou Ali Idris Sheikh, daya ne daga cikin mutanen da suka fi dadewa suna hidima a Masallacin Manzon Allah (SAW) da ke Madina.

Yanzu-Yanzu: Mutunen da ke kula da ƙabarin Manzon Allah ya rasu
Yanzu-Yanzu: Mutunen da ke kula da ƙabarin Manzon Allah ya rasu

Hukumar Gudanarwar Masallatan Harami ta sanar cewa, Agha Abdou Ali Idris Sheikh, ya koma ga Mahaliccinsa ne a ranar Litinin.

An gudanar da Sallar Jana’izarsa a Masallacin Manzon Allah sannan aka kai shi makwancinsa na karshe.

Abdou Ali Idris Sheikh shi ne Agha na uku da ya rasu cikin shekaru 10 da suka wuce.

A baya yawan masu aikin Agha ya haura mutum dubu daya, amma a halin yanzu wadanda suka rage a raye ba su fi biyar.







Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button