Matattu zasu iya jin maganar rayayyu su gane abinda ke faruwa da su – binciken likitocin jam’iyar New York


A yanzu nan Majiyarmu ta samu wani labari wanda shi wannan labarin ga wanda yake musulmi fiyayyen halitta Annabi Muhammad s.a.w ya fadi hakan inda wani mai amfani da kafar sada zumunta ya wallafa wannan rubutu mai suna Abba hikima.
Yanzu naga sakamakon wani binciken kimiyya da likitocin Jami’ar New York dake Amurka suka yi inda suka gano cewa mutanen da suka mutu na iya jin maganar rayayyu kuma suna iya gane abunda ke faruwa a tare da su.
Kafin wannan lokacin idan ka karantawa wadannan likitoci wadanda ba musulmi ba hadithan da Annabi SAWAW ya tabbatar mana shekara sama da 1400 cewa matattu na jin karar sawayen mutane a makabarta ko inda da kansa yake tambayar matattun mushrikai cewa ko sun samu alkawarin Allah bayan mutuwa gaskiya, har Sayyadina Omar yake tambaya cewa ya Annabi zai dinga magana da matattu, inda Annabi SAWAW yayi rantsuwa da Allah cewa; su da suke raye basu fi matattun jin maganarsa ba, cewa zasu yi karya ne.


Irin wadannan dalilai da suke bayyana daya bayan daya suka sa koda hankali da ilimin ka basu kai ka fahimci abu a addini ba, ko kuma abun ya saɓa da ma’aunin kimiyya, to ka sallama kabi kawai indai ya inganta. Saboda shi ilimin kimiyya, abune mai caccanzawa daga lokaci zuwa lokaci. Wanda yayi ka kuma, Masanin gaibu ne.
Allah kara mana shiriya. Allah barmu akan biyayya da sallamawa ga Annabi SAWAW.
Shafin da ke manhajar titkok mai suna @artificial.infusion Sunka wallafa wannan bidiyo.
Ga bidiyon nan .
@artificial.infusion Where does consciousness go after death? More curious, when does the human brain acquire consciousness? #conscious #life #death #afterlife #brightlight #heaven #hell #lifeafterdeath #universe #artificialinfusion #fyp ♬ original sound – Ai