Labarai

Tinubu ya naɗa shugabar sabuwar ma’aikatar taimakon al’umma

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da naɗin Delu Yakubu a matsayin shugaba ta farko a sabuwar ma’aikatar taimakon al’umma mai suna National Social Investment Programs Agency, NSIPA.

Wata sanarwa da mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai, Ajuri Ngelale ya fitar a yau Alhamis a Abuja, ta ce nadin ya dogara ne da amincewar majalisar dattawa.

Tinubu ya naɗa shugabar sabuwar ma'aikatar taimakon al'umma
Tinubu ya naɗa shugabar sabuwar ma’aikatar taimakon al’umma

An sanyawa dokar kafa Ma’aikatar Shirye-shiryen Taimakon Al’umma, NSIPA, (Establishment) Dokar, 2023, a ranar 22 ga Mayu.

Mrs Yakubu ta samu digirin digirgir a fannin aikin noma daga Jami’ar Jiha ta Fasahar Bio-Technology da ke Kharkiv, Ukraine, tare da gogewar sama da shekaru 15 a fannin Gudanar da Shirye-shiryen Taimakon Al’umma.

Shugaban ya umurci sabuwar shugabar da ta kasance jajirtacciya, nuna gaskiya, da samar da ayyuka masu inganci a NSIPA bisa kudurinsa na aiwatar da ajandar sabuwar rayuwa.







Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button