Kannywood

[Bidiyo] Duk randa Allah zai dauki ran Maryam Yahaya ina rokonsa ya dauka tare da nawa, Matashi

Wani matashi wanda ya bayyana kaunar da yake yiwa jarumar Kannywood, Maryam Yahaya a fili ya ce ba zai iya rayuwa a duniya ba idan jarumar bata raye.

Da haka ne yace yana fatan Ubangiji ya dauki rayuwarsa a ranar da zai dauki rayuwar jarumar.

A wani bidiyo na TikTok da matashin , an ga matashin yana bayyana sirrin da ke ransa.

Ya fara ne da cewa:

Hakika, gaskya ni bazan iya rayuwa babu Maryam Yahaya ba, ba wai kuma ina nufin a karkashin inuwata ba.

“Ba zan iya rayuwa ba muddin bana jin motsinta, ko da a birnin kif take. Shiyasa a ko da yaushe nake addu’a, duk ranar da Allah ya tashi daukar ran jaruma Maryam Yahaya, to ya dauka tare da nawa.

“Saboda idan babu Maryam babu ni.”

Ga bidiyon:

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button