Labarai

Daga ƙarshe dai an katse Layukan Sadarwa a jihar Katsina

Daga ƙarshe dai an katse Layukan Sadarwa a wasu sassan jihar Katsina

Daga ƙarshe dai an katse Layukan Sadarwa a wasu sassan jihar KatsinaA ƙalla ƙananan Hukumomi Goma Sha Ukku ne aka datse Layukan Sadarwasu a faɗin jihar Katsina a Yau ɗin nan, hakan kuma baya rasa nasaba da Yunƙurin da Gwamnatocin Arewachin ƙasar nan sukeyi na yaƙi da Ƴan Ta’adar Daji da suke addabar wannan yankin na Arewa maso yamma.
Ƙananan Hukumomin da Lamarin ya shafa sun haɗa da Sabuwa, Faskari, Dandume, Batsari, Danmusa, Kankara, Jibia, Safana, Dutsin-Ma da Kurfi waɗanda duk suke makwabtaka da dajin Ruggu Wanda ya kasance maboyar Ƴan Ta’adar Daji a faɗin jihar Katsina.
Sauran yankunan da Lamarin ya shafa sun haɗa da Funtua, Bakori da kuma Malumfashi.
Daily trust Idan dai ba’a manta ba a cikin Ƴan ƙwanakin nan ne akayi ta yaɗa wata Takardar da ta Ayyana cewa an ɗauke service na layukan Jama’a a faɗin jihar Katsina, Sanarwar da Hukumar da take kula da Kampanonin Sadarwa ta ƙasa ta musanta, Inda ta ayyana cewa Sanarwar ta jihar Zamfara ce ba ta jihar Katsina ba a wancen lokacin.
✍ Muhammad Aminu Kabir

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button