Labarai
Na amince da umarnin kotu na dakatar da muƙabala – Ganduje
Gwamnan ya bayyana hakan ne ta bakin Kwamishinan shari’a na jihar Barista Musa Abdullahi Lawal.
Kamar yadda Freedomradio na ruwaito.Kwamishinan ya ce, wannan Gwamnatin ba ta karya umarnin kotu, saboda haka za ta yi biyayya da umarnin musamman ganin kotun tana da hurumin bayar da shi.
Ya ci gaba da cewa, ai ba daidai ba ne a ce kotu ta bai wa Gwamnatin umarni kuma ta ƙi ba, a don haka yanzu babu batun zaman muƙabala ranar Lahadi.