Labarai

Bidiyo: Tawagar Gwannoni A Babbar Kasuwar Sokoto Sun Bada Tallafin Naira Miliyan Hamsin 50M

Maigirma Gwamnan jihar Sokoto Rt Hon Aminu Waziri Tambuwal CFR (Mutawallen Sokoto) ya jagoranci Tawagar Gwamnonin Plateau, Ekiti da Jegawa zuwa babbar kasuwar Sokoto, inda suka je wajen yin jaje ga gwamna Tambuwal da al’ummar jihar sokoto kan ibtila’in gobarar da aka yi a babban kasuwar inda aka yi hasarar dukiyoyin al’umma da dama.
Wanda a nan ce ciyaman na gidauniyar gwamnnonin Nigeriya sunka bada tallafi naira miliyan hamsin 50M domin taimakawa jaha da kuma yan kasuwa da sunkayi asarar dukiyoyinsu.
 
 
 
Maigirma Mataimakin Gwamnan jihar Sokoto Hon Dr Muhammad Manir Dan Iya (Walin Sokoto) kana Shugaban Kwamitin Gobarar kasuwa tare da ‘yan kwamitin sa ne suka tarbi Tawagar Gwamnonin a babbar kasuwar.
Maigirma Gwamna Tambuwal na tare da Rakkiyar kakakin Majalisar Dokoki ta jiha. Sakataren Gwamnati, Shugaban Ma’aikatan gidan Gwamnatin jiha, Shugaban Ma’aikatan gidan Gwamnatin jiha, Kwamishinoni da sauran su.

Majiyarmu ta samu muku wannan bidiyo daga shafin Bilya Yariman Barebarin Fcbk
Special Asst to Governor Tambuwal.

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button