Labarai

Tallafin Covid-19: An gane ba Buhari ne matsalar Najeriya ba (Hoto) – Zahra Buhari

 
Kwanaki kadan da suka gabata, ‘yan Najeriya sun gano ma’adanar da aka killace kayan abincin tallafin COVID-19 wanda CACOVID suka bayar, kuma sun fada gidajen sun kwashesu tas.
Majiyarmu ta samu daga Legit, Kayan tallafin sun hada da kayan abinci iri-iri wadanda ya kamata a rabawa talakawan Najeriya.
‘Yan Najeriya da dama sun yi ta caccakar gwamnatin jihohi a kan rashin raba kayan abinci da ya kamata su yi lokacin da aka shiga tsanani.

Wannan shine hoton da Hausaloaded na samu daga shafin zarah Buhari yi

Wata mai shirya fina-finai, Mansurah Isah, ta wallafa a shafinta na Instagram, inda ta nuna yadda aka gano kayan tallafin, wanda hakan ke nuna ba shugaban kasa ne matsalar Najeriya ba.
Zarah Buhari-Indimi, wacce diya ce ga shugaban kasa Muhammadu Buhari, ta kara wallafa wallafar Mansurah a shafinta na Instagram, da alamu ta yadda da abinda Mansurah Isah ta wallafa.

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button