Kannywood
Ali Nuhu Na Son a Buɗe Gidajen kallon fim
Fitaccen jarumin fina-finan Hausa na Kannywood Ali Nuhu ya buƙaci a diba buƙatunsu na buɗe wuraren kallon fina-finai a sinima.
Jarumin ya ce har yanzu ba su dalilin da ya sa gwamnati ba ta amince a buɗe wuraren kallon ba bayan kuma tuni aka buɗe wurare da dama da ke haɗa taron jama’a.
Ya ce dukkanin gidajen kallon sun ɗauki matakai na kariya amma ba wani ci gaba a tattaunawa da aka ɗauki lokaci ana yi tsakanin hukumomi da masu sinima.
Ya kuma ce suna jiran tallafin da gwamnati za ta ba masana’antarsu wadda ya ce ta samarwar miliyoyin ƴan Najeriya ayyukan yi a tsawon shekaru 20.
Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com