Labarai

Bidiyo : Kamin Gwamna Zulum ya je Baga, Sojoji sun Bashi Tabbacin cewa Babu Boko Haram a Garin ! Kalli Irin Cacar Baki Tsakaninsa Da Sojoji

Gwamnatin jihar Borno ta tabbatar da harin da aka kaiwa gwamnan jihar, Babagana Umara Zulum a jiya, Laraba a yayin da yake kan hanyar shiga Baga.

Me magana da yawunsa, Malam Isa Gusau ne ya tabbatar da haka ga BBChausa, yace kamin gwamnan yaje Baga, sojoji tun tuni sun bashi tabbacin cewa sun kwato garin Baga daga hannun Boko Haram.
Yace amma gwamnan ya bar Monguno yana kan hanyar zuwa Baga sai kawai suka fara jin harbin bindiga. Yace jami’an tsaron dake tare da gwamnan sun maida Martani inda wasu dake tawagar gwamnan suna bar wajan da rarrafe.
Yace gwamnan bai karasa garin na Baga ba, ya koma Monguno ya kwana.
5. Zulum was furious that despite huge number of the military presence in mile 4, which is only four (4) away from Baga, they couldn’t take over baga after one year. And his entourage was forced to retreat. pic.twitter.com/K3Rp9TnkiN

— Habu Kale Tijjani (@Habuhk4) July 30, 2020

Hakanan Hutudole ya samo daga shafin daya daga cikin hadiman gwamnan, Habu Kale Tijjani wanda ya bayyana hoton bidiyon da gwamnan ke caccakar sojojin da cewa babu alamar cewa suna aiki yanda ya kamaya.
Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button