Labarai

Sheik Mufti Menk Ya Kaiwa Sheik Pantami Ziyarar Ban Girma (Hotuna)

Shahararren Malamin addinin Musulunci Sheikh Mufti Ismail Menk malamin da ya yi sanadin musuluntar da dubbannin Turawa, ya ziyarci Maigirma Ministan sadarwa Dr Isah Ali Ibrahim Pantami har gidansa dake Abuja.

Idan Allah Ya kai mu gobe Asabar akwai wa’azozin da manyan Malaman addinin Musulunci za su gabatar a babban dakin taro na Kasa da Kasa dake Abuja cikinsu har da Maigirma Ministan sadarwa da sauran Malamai na kasashen waje

Ana gayyatar dukkan al’ummar Musulmin Nigeria da su halarci gurin wa’azin.
Allah Ya bamu ikon zuwa. Amin.

Daga Datti Assalafiy.

Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button