Kannywood

Na Yi Kuskure Da Na Shiga Siyasa, Yanzu Na Tuba – Adam A Zango

 

Adam Fitaccen jarumin Kannywood, Adam A. Zango, ya bayyana cewa, ya tuba daga shiga harkokin siyasa, domin ba karamin kuskure ya yi ba da ya shiga cikinta. Jarumin ya bayyana hakan ne a ranar Asabar, 23 ga Maris, 2019, ta Instagram dinsa, inda ya ce, “shiga harkar siyasa a wurina ba karamin kuskure ba ne, sabosa hakan ya janyo wasu masoyan nawa sun zama makiyana. Don haka Ina so in yi amfani da wannan lokaci na bai wa duk wadanda na bata wa rai hakuri. “Daga yanzu kuma zan mayar da hankalina kan sana’ata. Zan cigaba da kawo mu ku finafinai da wakoki masu kayatarwa. Ina son ku masoyana, don idan babu ku, ni ma babu ni.” Jarumin dai ya yi wannan sanarwa ne jim kadan bayan da sakamakon zaben cike gurbi na jihar Kano ke nuni da cewa, dan takarar da bai yi wa yakin neman zabe ba, wato Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na APC, shi ne a kan gaba. 

Gabanin fara zaben dai jarumin ya bayyana a wani hoton bidiyo ya na murna tamkar dan takararsa na PDP, Injiniya Abba Kabir Yusuf, zai lashe zaben, to amma sai labari ya nuna alamun shan bamban. Haka nan dan takararsa na kujerar shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar na PDP, shi ma ya sha kayi a hannun Shugaba Muhammadu Buhari na APC kafin gudanar da zaben gwamnoni. Adam Zango dai jarumi wanda ya saba fitowa ya ce ya bar wani abu da ya ke kan yi, inda hatta shi kansa fitowa a finafinai ya kan ce ya daina a wasu lokutan baya, ballantana kuma ita siyasar kasa. 
 
Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button