Addini

Ba Wanda Ya Kai Dan Bidi’a Wahalar Banza!!! -Dr Muhammad Sani Umar R/Lemo

Allah Ta’ala yana cewa, “Ka ce, ‘Shin in ba ku labarin wadanda suka fi kowa asarar ayyukansu. Su ne wadanda aikinsu ya bace a rayuwar duniya, alhali kuwa suna tsammanin suna kyautata ayyuka ne”.[Al-Kahfi, 103-104]. 

Magabata sun fassara wannan ayar da cewa, ana nufin Yahudu da Nasara, kamar yadda Sa’ad bn Abi Wakkas (R.A) ya yi. Yayin da shi kuma Sayyiduna Ali (R.A) ya fassara ta da cewa, su ne Khawarijawa. 
Imam As-Shatibi ya hade ma’anonin guda biyu, inda ya nuna cewa, ayar tana nufin duk wani mai aikata  bid’a a addini, sawa’un a cikin Yahudawa ne, ko a cikin Nasara ne, ko a cikin musulmi ne. Domin duk wanda yake bid’a yana daukan abin da yake yi abu ne mai kyau, tare da cewa, ya kaucewa hanyar da shari’a ta yarda da ita. 

Wannan magana ita ce, abin da Imamul Mufassirina Ibn Jarir At-Tabari ya bayyana a tafsirinsa. Allah ya tsare mu da aikin bid’a.

Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

One Comment

  1. These are really impressive ideas in regarding blogging.
    You have touched some fastidious points here. Any way keep
    up wrinting. It is perfect time to make some plans for the future
    and it’s time to be happy. I’ve read this post and if I could I wish to suggest you
    few interesting things or tips. Maybe you could write next articles referring
    to this article. I want to read even more things about it!
    Wow! This blog looks just like my old one!
    It’s on a completely different subject but it has pretty much the same layout and design.
    Great choice of colors! http://kuryaloaded.com

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button