Addini

“SHIN ‘DARIQA ‘KUNGIYA CE???” Ga AMSAR Daga Sheikh Usman Dahiru Bauchi Ya Bayar Kamar Haka karanta kaji


:
Tambayar Da Wani Bawan ALLAH Ya Yiwa LISANUL-FAIDHA(Maulanmu Shehu Dahiru Usman Bauchi(R.A) Kenan.
:
:
“Ita ‘DARIQA a ‘Lugga’ Tana Nufin Hanya, a ‘Istilahi’ Kuma Tana Nufin Riko Da Hanyar Bayin ALLAH Akan ‘Azkaransu’ Na Gyaran Zuciya Da Sharud’a, Ita ‘DARIQA Tana a ‘Muqamul Iman’ Ne Daga Cikin Hawa Uku Na Musulunci, Ita Hanya Ce(‘Dariqa) Wadda Zata Kai Ka Zuwa Wajen Neman Wani Abu Shi Ne; Zikirin ALLAH, Amma Ba Wai Ita Ce Manufa Ba, Kamar Masallaci Ne Da Sallah, Shi Masallaci Ba Shi Bane Manufar, Shi Matakala Ne Zuwa Ga Abin Nema Shi Ne Sallah, ‘DARIQA Ba ‘Kungiya Bace, In ‘Kungiya Ce To Waye Ne Chairman Na ‘Dariqa a Nigeria, Waye Sakatarenta, Waye Treasury Na ‘Dariqa(Na ‘Kasa) Duka Babu, ‘Dariqa Ba ‘Kungiya Bace Makaranta Ce Ta Gyaran Zuciyar ‘Dan Adam Kamar Yadda Mazhaba Ta Zamo Makaranta Ce Ta Fiqhu, To Haka Abin Yake”.
:
Mun Gode SHEHU(R.A)!
:
ALLAH Ya ‘Karawa SHEHU Lafiya Da Nisan Kwana, Ya Bamu Albarkarsu Don Alfarmar MA’AIKI(S.A.W). AMEEEEEN

Sources : fatyanul  islam of Nigeria 

Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button