Labarai

Sheik Sudais Ya Karrama Tsohon Gwamnan Sokoto, Bafarawa

Daga Ibrahim Baba Suleiman

Ministan Masallatayyan nan guda biyu masu Alfarma na Makkah da Madina, Sheikh Abdurrahman Sudais ya karrama tsohon gwamnan jihar Sokoto Alh. Attahiru Ɗalhatu Bafarawa a birnin Makkah.

Bafarawa ya samu Babbar kyautar ne daga minista Sudais lura da yadda Attahiru Bafarawa ya jajirce a wasu mihimman batutuwa a ƙasar saudiyya.

Bafarawa dai yana da kyakkyawar alaƙa da Sheikh Abdurrahman Sudais da mutunta juna, wanda a baya ma Bafarawa ya taɓa gayyatar Sheikh Sudais zuwa Sokoto domin buɗe wani katafaren masallaci da cibiyar musulunci a lokacin da yake Gwamnan Sokoto.

Haka Zalika sauran manyan Malaman Saudiyya da ɓangaren gwamnati suna girmama Bafarawa a duk lokacin da ya shiga Saudiyƴa, wacce har ta kai matuƙar Bafarawa yana Saudi to yana da wajen da hukumar masallaci ta ware masa a bayan liman domin girmamawa.

Wannan ba karamin alfahari bane ga ƙasar Nijeriya, ace ɗaƴa daga ciin ƴaƴanta ana girmama su a ƙasar Musulunci, kuma jagorar ƙasashen musulmi ta Duniya, wato Saudiyya.

Allah ya ƙarawa Ƙasar Nijeriya albarka, tare da ɗaga darajar ta tare da ƴaƴanta a idon Duniya. Amin.

Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button