Uncategorized

Fatawar Rabon Gado (99) – Dr Jamilu Yusuf Zarewa

Fatawar Rabon Gado (99)


Tambaya

Assalamu alaikum malam ya za’a raba gadon wanda ya mutu ya bar ‘ya’ya maza 9 da ‘yaya mata 8 da matan aure 2 da ‘yan’uwa shakikai?

Amsa

Wa alaiku assalam Za’a raba abin da ya bari gida:8, a bawa matansa kashi (1), ragowar kashi 7 sai a bawa ‘ya’yansa Maza da mata su raba, saidai kasancewar su (26) ne, tun da kowanne namiji yana matsayin mata biyu ne, za mu buga adadinsu (26) akan asalin (8) In da zai ba mu 208, sai mu bawa matansa daya cikin (8)dinta wato (26) ta in da kowacce mace za ta samu (13), ragowar sai mu bawa ‘ya’yansa, kowanne yaro zai samu (14), kowacce yarinya kuma za ta samu (7).

Allah ne mafi sani

Amsawa

DR JAMILU YUSUF ZAREWA

15/2/2017

Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button