Uncategorized

IDAN DREBA YA KASHE MUTANE BAKWAI,YAYA KAFFARARSA

IDAN DREBA YA KASHE MUTANE BAKWAI, YAYA KAFFARARSA ?

Tambaya:

Assalamu alaykum tambayata anan shine idan tsautsayi yasa Kai ajalin rai bakwai da motarka, idan zakai axumi na kaffara nawa zakai ?

Amsa:

To dan’uwa kisan kuskure yana wajabta abubuwa guda biyu:

1- Diyya wace dangin wanda ya yi kisan za su bayar ga dangin wanda aka kashe da kuskure, sai dai in sun yafe.

2- Kaffara, wacce zai ‘yanta kuyanga, in bai samu ba sai ya yi azumin wata biyu, kamar yadda aya ta 92 a Suratunnisa’i take nuni zuwa hakan.

Idan sama da mutum daya suka mutu a mota, ya wajaba ga Driban motar ya yiwa kowa kaffara kuma danginsa su biya diyya, mutukar shi ne sababi a hadarin, kamar ya zamana ya wuce danja ko kuma ya yi gudun da ya zarta ka’ida, ko burkinsa ya lalace amma ya ki gyarawa, ko wani abu makamancin haka wanda yake nuna sakacin Driba, ko wuce ka’idarsa.

Idan hadari ya faru wasu suka ji ciwo saboda sakacin Driba ko wuce ka’idarsa, sai suka mutu daga baya, danginsa za su biya diyyarsu kuma zai yiwa kowa kaffara, ko da kuwa bayan shekaru biyar ne da faruwar hadarin, saboda duk dalilin da yake kaiwa zuwa abu, to yana dai dai da abun

Allah ne mafi sani.

Don neman Karin bayani duba : Al’inaya 1116, Madalibu Uli-Annuhaa 6147 da kuma Fataawa Allajnah Adda’imah 23352.

Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
1772016

Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button