Ado Gwanja Babu abun da ya shiga tsakani na da Adam A.Zango kana na daina fitowa a matsayin dan daudu
Fitaccen jarumin wasan barkwanci kuma shahararen mawaki Ado Gwanjo, yayi karin haske game da alaka dake tsakanin sa da jarumi Adam A.Zango.
Jita-jitra dake yaduwa a kafafen sada zumunta na cewa jarumai suna takun saka tsakanin su.
Hirar shi da jaridar Premium Times, Ado Gwanja yayi karyata jita-jitan tare da bayana hakikanin alaka dake tsakanin sa da tauraron Kannywood.
Yana mai cewa ” Kasan ba a rasa wadanda basu rasa abin cewa a kullum. Su bi wurare suna fetsa maganganu iri-iri. Amma ni dai a sani na babu abin da ya shiga tsakani na da Adam Zango. Hasali ma shi maigida na ne domin ni a yaron sa na fara sana’a ta kuma har yan zu ma haka ne.
Jarumi wanda ya shahara wajen fitowa a matsayin dan daudu a fim, ya bayana cewa zai daina fitowa a matsayin haka. Yace daga yanzu matsayin barkwanci kawai zai dinga fitowa a cikin fina-finai.
” A’a yanzu kam na dai na fitowa a fina-finan da zai haska ni a matsayin dan daudu. Zan tsaya a barkwanci na kawai” yace.
Yayi ma dinbim masoyan sa godiya bisa soyayar da suka nuna masa game da wakokin sa kana yana masu albishiri cewa zai cigaba da nishadantar dasu.