Tuna Baya Matan Kannywood Da Suka Nishadantar Da Al’umma Shekarun Baya
Masana’antar Kannywood ta kai kusan shekara 20 da kafuwa kuma ta samu dinbim jarumai masu taka muhimmin rawa wajen nishadantar da al’umma.
A cikin tsawon shekarun da wannan dandalin ta samu asali an samu jarumai mata da dama da suka faranta mana rai da ire-iren rawar da suke takawa a idon telibijin.
Mafi yawancinsu a daina jin duriar su ne kasancewa shiga sahun gaba na rayuwar zamantakewar aure.
Domin martaba da raya wannan dandalin da take nishadantar damu a ko da yaushe bari mu waiwaya baya mu tuna wasu daga cikin tsofin jarumai mata gwarzaye da suka nishadantar damu shekarun baya kafin ire-iren su Hadiza Gabon da Rahama Sadau su amshi tutar raya masana’antar,
Saima muhammad
Saima muhammad tsohuwar jarumar masana’antar kannywood |
Abida muhammad
Abida muhammad tsohuwar jarumar kannywood |
Fati muhammad tsohuwar jaruma |
kafin shigowar wasu jarumai mata da ake damawa dasu a yanzu a wannan farfajiyar an samu wasu da dama wadanda har yanzu ,masoya da masu bibiyar fina-finai hausa suna kewar su.
Sadiya Gyale
Sadiya Gyale |
Safiya musa
Safiya musa Albarka Aure Tare da Danta |
Samira Ahmad |
Muhibbat abdulsalam
Albarkar aure tare da ‘ya’yanta |
Mansura isah tare Albarkacin aurenta |
Hafsat shehu ta farida jalal
Rukayya dawayya |
Wadannan sun tare da wasu da dama sun taka rawar gaske yayin da ake damawa dasu a harkar fim kuma sun taimaka wajen inganta ki’imar al’adar arewa ga bainar jama’a.
Muna musu fatan alheri tare da jinjina masu bisa gudummawar da suka bada a masana’antar kannywood.
Source : naij.com