Kannywood

Kannywood: Ina Matukar So Dana Ya Gaje Ni – Inji Sadiq Sani Sadiq


Fitaccen jarumin nan na wasan fina-finan Hausa mai suna Sadiq Sani Sadiq da wasu ke yi wa lakabi da dan marayan zaki ya fito fili ya shaidawa duniya cewa shi fa yana so dan sa ya gaje shi a harkar domin kuwa abun kirki ce.

Jarumin ya yi wannan ikirarin ne a cikin wata fira da yayi da majiyar mu da tayi da shi inda kuma ya bayyana sirrin sa da ya sa ya lashe babbar kyautar nan ta jarumin-jarumai har sau uku a jere.

NAIJ.com ta samu cewa jarumin ya bayyana cewa ba zancen alfahari ba amma idan dai har yana a cikin masana’antar ta fim to fa ba shakka shine zai cigaba da lashe kyautar don kuwa yana anfani da basira da kuma kwarewa sa sosai.

Haka nan kuma jarumin ya karyata rade-raden da ke yawo a gari na cewa wai yana so ne ya zarce manyan jaruman nan wato Adam A Zango da kuma Ali Nuhu inda yace su wadannan ai sarakai ne kuma wuri ake yi masu amma dai shi yana kokarin sa ne kawai.

Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button