Uncategorized

ABUBUWAN DA AKE SO MIJI YA FI MATARSA DA SU | DR JAMILU YUSUF ZAREWA

ABUBUWAN DA AKE SO MIJI YA FI MATARSA DA SU


Tambaya :
Aslkm, malam da fatan kana lafiya, wasu tambayoyi nake rokon Malam daya taimakamin da amsoshinsu in Allah yasa malam yasansu,

shin malam wai akwai wasu abubuwa uku da ake so mace tafi mijin da za ta aura da su,
sannan shima akwai abu guda uku da akeso ya fita da su?,
sannan akwai wadanda sukayi musharaka akansu, dafatan malam ya sansu, kuma za’a taimakamin da su.
nagode

Amsa :
To dan’unwa masana ilimin zamantakewar aure suna cewa, ana so mace ta fi mijinta da abubuwa uku : ta fi shi a kyau, ta fi shi kananan shekaru, ta fi son shi, sama da yadda yake sonta .

Ana so miji ya fi matarsa da abubuwa uku : ya fi ta kudi, ya fi ta ilimi, ya fi ta jarunta
Ana so su hadu a abubuwa uku : ya zama akwai yaran da yake hada su, ya zama addininsu daya, ya zama dukkansu suna son tarbiyya.


Idan aka samu wadannan uku-ukun, to za’a samu jin dadin aure.

DON NEMAN KARIN BAYANI KA NEMI SHIRIN DA NA YI A FREEDOM RADIO KANO, RANAR : 3 GA RAMADHAN 1434 H, A SHIRINSU NA MINBARIN MALAMAI
     Amsawa
Dr jamilu yusuf zarewa
Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button