Uncategorized

HUKUNCIN HADA SITTU SHAWWAL DA RAMUWAR RAMADAN|DR JAMILU YUSUF ZAREWA

HUKUNCIN HADA SITTU SHAWWAL DA RAMUWAR RAMADAN

Tambaya :
Malam idan ana binka ramuwar azimi za ka iya niyya biyu : wato da nufin sittu shawwal da ramuwar Ramadhana a guda daya ? don Allah mlm taimaka min da bayani.

Amsa :
To ‘yar’uwa kowanne daban ake yinsa, saboda manufarsu ta banbanta, don haka ba za’a hada su da niyya daya ba, kamar yadda ake yi a wankan janaba da wankan juma’a, za mu fahimci haka, a cikin fadin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi :

“Duk wanda ya azumci Ramadhana sannan ya biyar da kwanaki shida na Shawwal, Allah zai ba shi ladan wanda ya yi azumin shekara”
Muslim ya rawaito shi a hadisi mai lamba ta : 1164, kin ga wannan yana nuna Ramadan daban, sittu-shawwal daban.
Fadin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi :

” Sannan ya biyar da kwanaki shida na Shawwal” ya sa wasu malaman sun tafi akan cewa : bai halatta ayi sittu-shawwal ba, sai bayan an kammala ramuwar Ramadan. Kamar yadda ya zo a : sharhurmumti’i 6443

Allah ne ma fi sani

    Amsawa

Dr jamilu zarewa

Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button